--
Yanzu-Yanzu | Saudiyya Ta sanar da ganin Watan Ramadan:- Cikakken Bayanin kan Guzirin Masu Azumi.

Yanzu-Yanzu | Saudiyya Ta sanar da ganin Watan Ramadan:- Cikakken Bayanin kan Guzirin Masu Azumi.

>


 Guzirin Watan Ramadan

Marubuci :- Mahmud Isah Yola

Cikin ta ana buɗe ƙofofin Aljannah don

masu shiga, ana kulle ƙofofin wuta Saboda

ba’a fatan a samu masu shiga.

Shaiɗanu masu umurtan mutane da

miyagun ayyuka an ɗaɗɗaure, ko wani

dare Allah yana ‘Yanta dubban bayi ya

musu kyautar Aljannah ya kuma amintar

dasu daga Wuta , a cikin ta akwai wani

dare, da ibada a cikin shi yana dai-dai da

ibadan shekara tamanin da ‘Yan Kai.

Ya kai Mai fatar rahamar ubangijinsa ,

yawaita ayyukan alkahairai cikin wata



domin samun yardan ubangijinka.

Ya kai mai aikata saɓo ko laifi, ka sani ya

wajaba a kanka ka bari cikin wannan

wata , in har ko ka ƙi, tsinuwan Manzon

Allah (S.A.W) ta tabbata a kanka, duk

wanda annabi ya tsine masa kuwa ya

halaka.

Wani al’amari na musamman:

Allah ta’ala na cewa:

”Lallai mun saukar da wannan Kur’ani

cikin dare mai albarka………. A cikin ta ake

rarrabe dukkan al’amari…”

Suratud Dukhan.

Wannan aya Malaman tafsiri sukace:

Tana nuna cikin Ramadan ake ƙaddara

abubuwan da zasu auku ga bayi a shekara,

na alkhairi ko sharri.

Saboda haka ka dukufa wajen addu’an

Allah ya sada ka da alkhairan da kake

buƙata, ya kuma kare ka daga sharrin da

kake tsoro.

Addu’ar mai azumi karɓaɓɓiya ce.

Kenan za’a baka alkhairan da ka nema , a

kuma kare ka sharrin da ka nemi tsari

daga gare shi.

Ya Allah ka sada mu da alkhairan wannan

wata , ka kare mu dukkan sharri, ka kuma

buga mana hatimin ‘Yan aljannah Amin.

Copied👇

 UUsman Adam AhmadAUsman Adam AhmadAUsman Adam Ahmad

0 Response to "Yanzu-Yanzu | Saudiyya Ta sanar da ganin Watan Ramadan:- Cikakken Bayanin kan Guzirin Masu Azumi."

Post a Comment