--
Rarara Yayi Cikakken Bayani Kan Musabbabin Rikicinsa Da Gwamnan Kano.

Rarara Yayi Cikakken Bayani Kan Musabbabin Rikicinsa Da Gwamnan Kano.

>

 






Cikin Wani Bayani Da Muka Samu Daga Bakin Abis Fulani Wanda Ya Tabbatar Da Ya Samo Shi Ne Daga Majiya Mai Tushe Cewa.


Musabbabin Rikin Mawakin Da Gwamnatin Jahar Kano Shine, Rarara Ya Bukaci Da Abaiwa Wasu Daga Cikin Yan Kannywood Takara.


Ya Bukaci Abaiwa Abale Dakuma Aminu Ladan Wasu Kujeru A Jam'iyyar APC.


Bayan Da Aka Ki Bayarwa Ne, Sai Rarara Yace Zaiyi APC A Sama Amma Bazaiyi APC A Kano Ba.


Lamarin Da Ya Fusata Gwamnan Jahar Kano Abdullahi Umar Ganduje, Wanda Harma Ya Cire Shi Daga Cikin Masu Kamfen Din Bola Tunubu.


Kamar Yadda Zaku Kalli Bidiyon A Kasa, Andai Tasamun Cece Kuce, Wanda Harma Ake Rade Radin Za'a Rushe Gidan Mawakin.


Mutane Da Dama Dai Na Ganin Laifin Yan Siyasar Jahar Kano, Wajen Bawa Mawakin Damar Da Ta Wuce Gona Da Irin Na Cin Mutumcin Manya A Jahar.


Adai Yan Kwanakin Nan Mutane Da Dama Sunyi Kiraye Kiraye Da A Takawa Mawakin Birki Kan Cin Mutum Cin Manyan Mutane Musamman Ma Yan Siyasar Jahar

0 Response to "Rarara Yayi Cikakken Bayani Kan Musabbabin Rikicinsa Da Gwamnan Kano. "

Post a Comment