--
DADUMINSA, Ajilesoro ya lashe kujerar majalisar wakilai ta Ife a PDP

DADUMINSA, Ajilesoro ya lashe kujerar majalisar wakilai ta Ife a PDP

>

 




Ajilesoro ya lashe kujerar majalisar wakilai ta Ife a PDP


Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa, INEC, ta bayyana Taofeek Ajilesoro na jam’iyyar PDP a matsayin wanda ya lashe zaben mazabar tarayya ta Ife a ranar Asabar.


Jami’in zabe na INEC, Farfesa Abdulfatai Makinde ne ya bayyana Ajilesoro, wanda ya samu kuri’u 53,078 a matsayin wanda ya lashe zaben a babban dakin tattara sakamakon zaɓe na Ife a yau Lahadi a Ile-Ife.


Mista Makinde ya ce dan takarar jam’iyyar APC, Benjamin Adereti, ya samu kuri’u 51,051.


Ajilesoro dan majalisar wakilai ne, mai wakiltar mazabar tarayya ta Ife a majalisar wakilai.

SOURCE /CREDIT/Daily Nigerian Hausa via Facebook search. 

0 Response to "DADUMINSA, Ajilesoro ya lashe kujerar majalisar wakilai ta Ife a PDP"

Post a Comment