--
Ankama Matar Auren Da Take Zinah Da Ɗan Ta’adda Kuma Take Kai Musu Bayanan Sirri

Ankama Matar Auren Da Take Zinah Da Ɗan Ta’adda Kuma Take Kai Musu Bayanan Sirri

>


 Ankama Matar Auren Da Take Zinah Da Ɗan Ta’adda Kuma Take Kai Kusu Bayanan Sirri


Kamar Yadda Shafin Hausaloaded Ya Rawaito Ankama Wata Matar Aure Tana Zinah Da Da Bindiga Kuma Tana Kai Musu Bayanan Sirri.


Yadda Maryam Abubakar Matar Aure Ke Kwanciya Da Dan Bindiga, Sannan Takai MusuWasu Matan Zuwa Cikin Daji Tare Sauran Ababen More Rayuwa


A cikin shekara ta 2021 kadai, yan bindiga dake ayyukan taaddanci a sassa daban-daban naArewacin Najeriya musamman a yankin Arewa maso Yamma, sun kashe gomman mutane, tareda lalata dukiyoyi na miliyoyin Naira.


Yan bindigar sun kuma yi awon gaba da yara yan makaranta da yawa, tare da neman kudin fansadomin sako su.


Yan bindigar sun kuma mayar da yankin ya zamawuri mafi rashin tsaro a kasar.



Abin bakin ciki,duk da haka, wasu matan da ya kamata sufahimci irin barnar da yan bindigar keyi musamman yadda ayyuka yan bindigar suka shafi mata da yara, haka wasu matan irin su Maryam suka rufe ido suka cigaba da yi wa kungiyoyin masu dauke da makaman aiki.


Wani abin damuwa ma shi ne, matar aure da aketsammanin ta zama uwa ta gari, itace yanzu taiya kulla yin soyayya da daya daga cikin yanbindiga dake dajin Kaduna, ta kuma wadata suda yan uwanta mata don jin dadi.


Idan ba a manta ba a safiyar yau ne wani rahotoda gidan Talabijin na Channels TV ya fitar, yabayyana cewa kakakin rundunar ‘yan sandan Najeriya Frank Mba ya bayyana kama wata mataraure mai shekaru 39 mai suna Maryam Abubakar, wacce saurayinta dan bindiga ne dukda cewa tana da aure.


Rahoton yace, Maryam wadda mijinta yana rayekuma yana gida, tana saduwa da daya daga cikinyan bindigar, tare da wasu matan sannan sunakai musu abinci, da kayayyakin more rayuwa dayan mata don jin dadi.


Har ila yau, suna taimaka wa ‘yan bindigar wajengudanar da bincike, da kuma ba su bayanai kanwani abin da aka sa a gaba wanda yin haka hakika wannan wani zagon kasa ne ga yakin dagwamnati ke yi da rashin tsaro a kasa.



Mutane irin su Maryam Abubakar da ke aiki dayan bindiga, ko dai a matsayin masu ba dalabari, ko kuma masu kawo kayayyaki, sunazagon kasa a yakin da gwamnati ke yi da rashintsaro a kasar.


Za a iya cewa, kayayyakin da mutane irin suMaryam suke kaiwa yan bindigar ne ya sa ‘yanta’addan masu dauke da makamai samun saukinrayuwa a cikin dajin.


Har ila yau, idan ba tare da bayanai da abubuwanda mutane irin su Maryam, da sauran masu ba dalabari suka ba wa wadannan ‘yan bindiga ba, ‘yanbindigar ba za su iya rayuwa ba na dogon lokacia cikin daji Kamar Yadda Majiya jaridar Sokkoto Ta Wallafa.

0 Response to "Ankama Matar Auren Da Take Zinah Da Ɗan Ta’adda Kuma Take Kai Musu Bayanan Sirri"

Post a Comment