--
Yanzu-Yanzu: Kasa ta rufta da mutane dayawa masu hakar zinari a Nijar

Yanzu-Yanzu: Kasa ta rufta da mutane dayawa masu hakar zinari a Nijar

>



Rahotannin da ke shigo mana yanzu haka sun tabbatar mana da cewa kasa ta rufta da mutane masu hakar Zinare marasa adadi a jihar Maradi da ke Jamhoriyar Nijar.

Yanzu haka da ranar nan ana can ana aikin tono gawarwakin mutanen da kasa ta rufta da su a jihar Maradi ta Nijar da ke aikin hakar Zinare.

Kawo yanzu mun samu labari cewa akwai 'yan Najeriya su 6 daga karamar hukumar Gudu ta jihar Sokoto a cikin wadanda lamarin ya rutsa da su.

Wannan dai shine karo na biyu da kasa take ruftawa da masu aikin hakar zinare a jihar ta Maradi.

Ko a kwanan baya sama da mutun 100 ne su ka rasa rayukkan su a wajen wannan aiki

0 Response to "Yanzu-Yanzu: Kasa ta rufta da mutane dayawa masu hakar zinari a Nijar"

Post a Comment