--
Albashin Gwamnatin tarayya Na N5000 Duk wata, ya fara samun Mutanen jihar Jigawa

Albashin Gwamnatin tarayya Na N5000 Duk wata, ya fara samun Mutanen jihar Jigawa

>


An yi murna da farin ciki ga dubban mazauna jihar Jigawa a jiya yayin da gwamnatin tarayya ke ci gaba da raba kudade na Naira 5,000 duk wata a jihar.


Bisa ga rijistar jin dadin jama’a na jihar, sama da mazauna kasa 167,620 ne ake sa ran za su karbi kudin da ya kai Naira biliyan 1.6.


A ziyarar da wakilinmu ya kai wasu wuraren biyan kudi a karamar hukumar Kiyawa ta jihar, ya ga daruruwan wadanda suka ci gajiyar shirin sun yi tattaki zuwa wurin da katunansu domin biyan su.


A cewar daya daga cikin wadanda suka ci gajiyar tallafin, Hajara Rabi’u, kudin naira 5,000 duk wata ya canza rayuwarta da ta danginta.


“Na tsufa da ba zan iya fara kowace sana’a ba, abin da nake bukata a yanzu shi ne abin da zai sa raina da jikina su hadu a sauran kwanakin da suka rage a duniya, na gode wa Allah da wannan Naira 5,000 ya ba ni sauki,” inji ta.


Jami’in bayar da horo da sadarwa na jihar, Malam Mustapha Yakubu Madobi, ya ce ana ci gaba da gudanar da atisayen biyan na watan Mayu da Yuni.


Ya kara da cewa, gwamnatin tarayya ta baiwa kamfanoni biyu kwangilar biyan kudaden, kuma kamfanin na farko ya biya wadanda suka ci gajiyar tallafin su 67,402, yayin da ake ci gaba da biyan ma’aikata 91,255 a fadin jihar.


©Ahmed El-rufai Idris

0 Response to "Albashin Gwamnatin tarayya Na N5000 Duk wata, ya fara samun Mutanen jihar Jigawa"

Post a Comment