
An Gayyato Zakir Naik Kan Yazo Yayi Wa'azi A Gasar Cin Kofin Duniya Na FIFA A Qatar
Sunday 20 November 2022
Comment
An Gayyato Zakir Naik Kan Yazo Yayi Wa'azi A Gasar Cin Kofin Duniya Na FIFA A Qatar
Ƙasar Qatar ta gayyaci sanannen malamin addinin musuluncin nan mai da'awa wato Sheikh Zakir Naik domin ya riƙa gudanar da karatuttuka na kira zuwa ga musulunci.
Haka nan malamin zai kuma ƙara bayyana ma duniya ainihin yadda addinin yake saɓanin yadda akan yaɗa a wasu kafafen sadarwa musamman ma kafafen sadarwar ƙasashen Yamma.
Zakir Naik dai zai kasance a Qatar har zuwa ƙarshen wasan na FIFA na bana, wanda yanzu haka ma ya isa ƙasar.
Muna fatan Allah ya ƙara ɗaukaka addinin Musulunci da Musulmi.
SOURCE 👇
Mikiya Hausa Labarai 24 on Facebook.
0 Response to "An Gayyato Zakir Naik Kan Yazo Yayi Wa'azi A Gasar Cin Kofin Duniya Na FIFA A Qatar"
Post a Comment