--
Hukumar ‘Yan Sandan Najeriya zata sake daukar sabbin ma’akata guda dubu 20

Hukumar ‘Yan Sandan Najeriya zata sake daukar sabbin ma’akata guda dubu 20

>


Hukumar Jami’an tsaron ‘yan sandan Najeriya ta bayyana cewa za ta sake daukar sabbin ma’aikata a wannan shekara ta 2022.

Shugaban Hukumar IGP Usman Alkali ya bayyana wa DW Hausa cewa akalla zasu sake daukar sabbin ma’akata guda dubu ashirin 20.

Wannan ya biyo bayan karancin jami’an tsaro da ake samu a sassan kasar nan, inda za a Kara su domin bada tsaro ga al’umma Kasa.

Sai dai IGP ya bayyana cewa nan ba da jimawa ba za su sanar da matasa hanyoyin da zasu bi wajen samun aiki a wannan hukuma ta jami’an tsaron ‘yan sanda.


Cikakken Rahoto na Nan tafe...

0 Response to "Hukumar ‘Yan Sandan Najeriya zata sake daukar sabbin ma’akata guda dubu 20"

Post a Comment