--
DA DUMINSA: Sojojin Najeriya sun Hallaka kwamandan ‘yan ƙungiyar ISWAP a jihar Borno

DA DUMINSA: Sojojin Najeriya sun Hallaka kwamandan ‘yan ƙungiyar ISWAP a jihar Borno

>



Rahotannin da ke shigo mana sun nuna cewa jami’an tsaron Sojojin Najeriya, sun yi nasarar kashe miyagun ‘yan ƙungiyar ISWAP da dama sun Kuma kashe babban kwamandansu a jihar Borno.

Lamarin ya faru ne a ranar Lahadi 13 ga watan Fabrariru na Shekarar 2022, a wani harin kwantan bauna da suka Kai masu. 

An samu tabbacin cewa sojojin Najeriya sun kai farmakin  a jirgin A-29 Super Tucano a ranar 13 ga Fabrairu, 2022, sun kashe babban kwamandan ISWAP, Malam Buba Danfulani da wasu mayaka da dama a gefen tafkin Chadi a karamar hukumar Kukawa da ke jihar Borno. 

0 Response to "DA DUMINSA: Sojojin Najeriya sun Hallaka kwamandan ‘yan ƙungiyar ISWAP a jihar Borno"

Post a Comment