--
Shin da gaske ne za'ayi amfani da Network 5G a Najeriya? Duba amsar da Dr. Pantami yabayar

Shin da gaske ne za'ayi amfani da Network 5G a Najeriya? Duba amsar da Dr. Pantami yabayar

>


Minista Pantami ya ce saura kiris 5G ya fara aiki a Najeriya


Gwamnatin Najeriya ta shirya tsaf domin fara dasa cibiyar sadarwar 5G a cikin Najeriya Ministan sadarwa da tattalin arzikin zamani, 


Dr Isa Ali Pantami ne ya bayyana hakan ga NAN Wannan na zuwa ne bayan gudanar da cikakken bincike ta fuskoki da yawa in ji Dr Pantami 


Abuja - Gwamnatin tarayya ta ce nan ba da jimawa ba za ta dasa cibiyar sadarwa ta 5G a cikin kasar don kara gudun cudanyar yanar gizo, in ji TheCable. 


Ministan sadarwa da tattalin arzikin zamani Isa Pantami ne ya bayyana hakan a Abuja lokacin da yake zantawa da kamfanin dillancin labarai na Najeriya (NAN). 


Pantami ya ce shawarar dasa cibiyar sadarwa ta 5G ta biyo bayan sakamakon cikakken bincike, kwakwaf da gwajin kawar shakku kan barazana ga tsaro ko kiwon lafiya. 


Ya yi bayanin cewa aiki kan manufofin kasa na 5G ya kai 95% kuma za a gabatar da shi ga majalisar zartarwa ta tarayya (FEC) a kan kari. 


Pantami, wanda ya ce babban abin da ya fi damun gwamnati shi ne tabbatar da tsaro da walwalar ‘yan Najeriya wajen amfani da ayyukansu a bangaren sadarwa, ya dora laifin jinkirin da aka samu na dasa cibiyar sadarwa ta 5G kan wasu makiran shakku da ake yadawa. 


A cewarsa: “Gwamnatin mu mai sauraran mutane ce; don haka muna sauraron sukar da ta dace, muna girmama hakan kuma muna yabawa kuma akalla muna kimanta aikatawa. 


"Mun kai kololuwar mataki kan 5G, to, wani batun ya taso cewa 5G yana da alaka da Korona; mutane da yawa ciki har da masu ilimi sun fara yayata batun ba tare da tantancewa ba. 


“A zahiri, mutane sun dan tsorata kuma suna shakkar fasahar. 


"Don haka mun ba da isasshen lokaci don yin karin shawarwari, kirkirar shirin wayar da kan jama'a a cikin yarukan gida don wayar da 'yan kasar mu saboda magance duk wani kalubale. 


“Mun kafa wata tawaga ta fasaha wacce ta dace da tsaro, kiwon lafiya da cibiyoyin muhalli da kuma ma’aikatan gwamnati domin mu kasance a bangare daya. "Ina so in ba ku tabbacin cewa cibiyar sadarwar 5G tana cikin tsarin sanarwa mai kyau." 


An fara batun kasuwancin 5G da hukumar NCC Pantami ya ce ma’aikatar sadarwa ta fara tattaunawa da Hukumar Sadarwa ta Najeriya (NCC) game da kasuwancin cibiyar sadarwar 5G, Punch ta tattaro. 


“Daga wannan gaba, NCC za ta ba masu gudanar da ayyukan wayoyin hannu don fara dasawa; don haka, aikin kusan a shirye yake. "Na je Majalisar kasa, na kare gabatarwar mu kuma sun yarda, sun kuma amince da dasa 5G 


"Sun kuma karfafa mana da mu yi koyi da wasu kasashe wadanda suka dasa 5G kuma mun riga mun yi hakan. "Hukumar Lafiya ta Duniya ta fitar da sanarwa cewa babu wata alaka tsakanin cibiyar sadarwar 5G da Korona kuma hakan na magance matsalar lafiya. 


"Hakanan, Kungiyar Sadarwa ta Duniya (ICU), wacce reshen Majalisar Dinkin Duniya ce, ita ma ta fitar da wata sanarwa da ke karyata duk wani tasirin sharri daga 5G." 


Source: Legit

0 Response to "Shin da gaske ne za'ayi amfani da Network 5G a Najeriya? Duba amsar da Dr. Pantami yabayar"

Post a Comment